DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fursunoni 68 ne suka samu nasara a jarabawar NECO ta 2025 a jihar Kano

-

Hukumar kula da gidajen gyaran hali ta Nijeriya reshen jihar Kano, ta bayyana cewa fursunoni 68 sun samu nasara a jarabawar NECO ta shekarar 2025.

Mai magana da yawun hukumar a jihar, CSC Musbahu Lawan, ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano a ranar Litinin.

Google search engine

Ya ce wannan nasara ta samu ne sakamakon ingantaccen tsarin koyarwa na cibiyar gidajen gyaran hali da kuma cikakken tallafin gwamnatin Jihar Kano.

A cewarsa, shirin ya nuna yadda ake aiwatar da dokar Correctional Service Act ta shekarar 2019, wacce ta bai wa fursunoni damar koyon karatu da sana’o’i a gidajen yari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara