DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kasashen kungiyar AES sun fice daga kotun ICC

-

 

Kasashen kungiyar AES sun ayyana ficewarsu daga kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa wato ICC.

Google search engine

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da shugaban kungiyar, kuma shugaban kasar Mali, ya rattaba wa hannu a ranar 22 ga watan Satumba, kasashen uku na yankin Sahel da ke karkashin mulkin soja sun bayyana hakan bayan wasu zarge-zarge da suka yi wa kotun.

Daga cikin zarge-zargen da kasashen suka yi har da ikirarin cewa kotun ta kasa gurfanar da wasu da suka kira shafaffu da mai ne, wadanda suka fi karfin doka duk kuwa da laifukan da ake zarginsu da aikatawa.

Haka kuma, kasashen sun zargi kotun da zama ’yar amshin shatar wasu kasashen turawan mulkin mallaka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara