DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zan kare muradun Yarbawa idan na ci zaben shugaban kasa – Atiku Abubakar

-

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi alkawarin sanya muradun al’ummar Yarbawa a saman jerin ajandar mulkinsa idan ya lashe zaben shugaban ƙasa na 2027.

Atiku ya musanta maganganun da ake yadawa cewa mulkinsa zai bada fifiko ga Hausa/Fulani a kan Yarbawa ko sauran kabilun Nijeriya.

Google search engine

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Kola Johnson, ya fitar a Abuja ranar Alhamis, Atiku ya ce yana da zumunci mai karfi da Yarbawa da iyalai da abokan arziki.

Don haka ya kara da cewa, alaƙar aure kadai ta isa ta kawar da duk wani tsoro ko fargaba na cewa mulkinsa zai kawo wariya da ƙabilanci tsakanin kabilun kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara