DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kamfanoni ne ginshiƙin ci gaban tattalin arzikin Najeriya – Sarki Sanusi

-

Muhammadu Sanusi II, ya yi wannan bayani ne a yayin wani taron koli da aka gudanar a gefen taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 da aka gudanar a birnin New York, ranar Laraba.

Sarkin na Kano ya ce bude kofar saka hannun jari daga ‘yan kasuwa shine ginshiƙin da zai buɗe damar Tattalin arzikin ƙasar da kuma ci gaba da tabbatar da sauye-sauyen da ake yi a halin yanzu.

Google search engine

Rahoton jaridar Punch ya Ambato shi yana bayyana cewa dole ne a baiwa ɓangaren masu zaman kansu muhimmiyar dama wajen habbaka ci gaba da jawo hannayen jarin da ake buƙata don sauya Tattalin arzikin ƙasar.

Taron, wanda aka yi wa taken “ƙarfafa zuba jari don ci gaba da musayar al’adu,” ya gudana ne a dakin taro na Henry George School of Social Science da ke Manhattan, Amurka, karkashin wata sanarwa da shugaban jam’iyyar APC reshen Amurka, Farfesa Tai Balofin, ya fitar ranar Laraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara