Shugaban karamar hukumar Ifelodun a Jihar Kwara, Hajji AbdulRasheed Yusuf, ya bayyana cewa sama da kashi 98 cikin 100 na waɗanda ake sacewa a Kudancin jihar Fulani ne, ba Yarbawa ba kamar yadda ake yawan yadawa.
Yusuf ya yi wannan bayani ne a yayin shirin “Newskeg” na kungiyar ɗaraktocin ƙungiyar ƙwararrun ƴan jarida ta Najeriya (NUJ) da aka gudanar a sakatariyar hukumar a Ilorin.
Ya ce akwai damuwa sosai yadda hukumomin tsaro sukan tabbatar wa da hukumar cewa mafi yawan waɗanda ake yin garkuwa da su a yankin Fulani ne.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito shi ya kuma bayyana cewa masaniyar sirri ta nuna cewa masu ba barayin bayanai na fakewa ne a kasuwannin shanu na jihar.
Ya ƙara da cewa, a baya shugabannin kananan hukumomi bakwai na yankin Kwara ta Kudu sun yanke shawarar rufe dukkan kasuwannin shanu, amma daga baya suka janye wannan mataki.



