DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fulani ake sacewa fiye da Yarbawa a jihar Kwara – Shugaban karamar hukuma

-

Shugaban karamar hukumar Ifelodun a Jihar Kwara, Hajji AbdulRasheed Yusuf, ya bayyana cewa sama da kashi 98 cikin 100 na waɗanda ake sacewa a Kudancin jihar Fulani ne, ba Yarbawa ba kamar yadda ake yawan yadawa.

Yusuf ya yi wannan bayani ne a yayin shirin “Newskeg” na kungiyar ɗaraktocin ƙungiyar ƙwararrun ƴan jarida ta Najeriya (NUJ) da aka gudanar a sakatariyar hukumar a Ilorin.

Google search engine

Ya ce akwai damuwa sosai yadda hukumomin tsaro sukan tabbatar wa da hukumar cewa mafi yawan waɗanda ake yin garkuwa da su a yankin Fulani ne.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito shi ya kuma bayyana cewa masaniyar sirri ta nuna cewa masu ba barayin bayanai na fakewa ne a kasuwannin shanu na jihar.

Ya ƙara da cewa, a baya shugabannin kananan hukumomi bakwai na yankin Kwara ta Kudu sun yanke shawarar rufe dukkan kasuwannin shanu, amma daga baya suka janye wannan mataki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara