Uwargidan shugaban Najeriya Sanata Oluremi Tinubu, ta ce ta yafe wa duk wani da ya ci amanar magidanta shugaba Bola Tinubu a lokacin zaben 2023.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa, Oluremi Tinubu ta bayyana haka ne a cikin wani sabon littafinta mai shafi 52, wanda ta wallafa a lokacin bikin cikar ta shekaru 65.
A cewar ta, ba ta da matsala da kowa saboda ta zabi zaman lafiya fiye da komai.



