Ministan Abuja Nyesom Wike ya ce babban birnin na daga cikin wurare mafiya kwanciyar hankali a Najeriya.
Wike ya bayyana haka ne ta cikin sakonsa na taya Najeriya murnar samun ‘yancin kai, yana mai yaba wa mazauna birnin wajen rungumar zaman lafiya, duk da cewa akwai matsaloli ‘yan kalilan.
A cewar Wike, samun wannan yanayi ya kasance sakamakon hadin kai da aka samu daga bangaren gwamnati da kuma mazauna birnin, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.



