Babban sufeton ‘yan sandan Najeriya Kayode Egbetokun ya bayyana cewa daga ranar Alhamis 2 ga watan Oktoba, jami’ansu za su fara kamen masu amfani da bakin gilashin mota ba tare da izini ba a fadin kasar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ta kasa ASP Mohammed Halima ta fitar, kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito.
Sanarwar ta bayyana cewa matakin na kan tsarin dokar haramta amfani da bakin gilashin mota ta shekarar 2004, a yunkurin tabbatar da zaman lafiya da magance ayyukan laifi.
Haka kuma, ta ce wa’adin da aka bai wa masu motoci domin sabunta takardun izini ya kare, saboda haka wajibi ne kowa ya bi doka.



