Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri ya yi wa wasu daurarru 6 da ke tsare a gidan gyaran hali na jihar afuwa albarkacin ranar ‘yancin kan Najeriya.
A cikin jawabinsa a ranar Laraba, Fintiri ya ce alamun cigaba da kuma inganci a halayyar mutanen, ya sanya suka shiga cikin yafiyar.
Wadanda aka yi wa afuwar sun hada da Abraham Marksunil, David Paul, Ibrahim Adamu, Usman Inuwa da Sani Yahaya.



