Kwamitin majalisar wakilan Najeriya mai bibiyar kundin tsarin mulki zai zauna da jam’iyyun siyasa masu rajista a fadin kasar, don tattauna batun yin kwaskwarima a kundin.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa kwamitin karkashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar Benjamin Kalu, za su duba batutuwan da suka shafi ‘yansandan jihohi, ‘yancin gashin kananan hukumomi, samar da muhimman gurabe ga mata a tsarin gudanarwa da dai sauran su.
Za a yi zaman tattaunawar ne tsakanin bangarorin biyu a ranar Litinin, 6 ga watan Oktoban 2025.



