DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar ASUU ta janye yajin aikin gargadin da ta tsunduma

-

Kungiyar malaman jami’o’i ta Nijeriya ASUU ta janye yajin aikin gargadin da ta tsunduma.

Shugaban kungiyar Farfesa Chris Piwuna ne ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai da ya gudana a ranar Laraba, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

Labari mai alaka: ASUU ba ta da hujjar shiga yajin aiki domin mun biya dukkanin bukatunta – Gwamnatin Nijeriya

A cewar sa, daukar matakin ya biyo bayan wani zama da kwamitin zartarwar kungiyar ya gudanar, bayan samun martani daga bangaren gwamnati kan bukatunsu.

Haka kuma, ASUU ta ce iyaye, dalibai da kuma kungiyar kwadago ta NLC sun taka rawar gani wajen sake bibiyar yajin aikin gargadin da ta yi niyyar gudanarwa na tsawon makonni biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon Minista Tanimu Turaki ya zama ɗan takarar shugabancin jam’iyyar PDP na Arewa

Jagororin jam’iyyar PDP na yankin Arewacin Nijeriya sun amince da tsohon Ministan Harkoki. A Musamman, Tanimu Turaki (SAN), a matsayin ɗan takarar da suka amince...

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

Jam'iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami'anta guda takwas, bayan samun...

Mafi Shahara