DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar Tarayya ta amince da ƙirƙirar sabbin jihohi guda shida a Nijeriya

-

Kwamitin haɗin gwiwa na Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai mai kula da gyaran kundin tsarin mulki ya amince da ƙirƙirar sabbin jihohi guda shida a Nijeriya.

Kamar yadda rahoton ya nuna, wannan shawara ta fito ne daga taron kwana biyu da aka gudanar a birnin Legas, ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, da mataimakin kakakin majalisar wakilai, Benjamin Kalu.

Kwamitin ya tattauna kan ƙuduri 69, buƙatun ƙirƙirar jihohi 55, gyaran iyakokin jihohi biyu, da kuma buƙatun ƙirƙirar ƙananan hukumomi 278 yayin taron.

A yayin zaman ranar Asabar, mambobin kwamitin sun amince da ƙirƙirar jihohi shida sabbi, kuma idan majalisar ta amince da wannan mataki gaba ɗaya, adadin jihohi a Nijeriya zai ƙaru daga 36 zuwa 42.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

ADC ta sake tabbatar da Sufiyanu a matsayin shugaban Kebbi, wani tsagi ya nuna turjiya

Ƙungiyar Shugabannin Jam’iyyar ADC a Jihohin Najeriya ta sake tabbatar da Engr. Bala Sufiyanu a matsayin sahihin shugaban jam’iyyar na jihar Kebbi, daidai lokacin da...

Farashin shinkafa ya karye a kasuwannin Legas

Farashin shinkafa ya sauka sosai a kasuwanni da dama na birnin Legas, sakamakon yawaitar shigowar shinkafa ta kan iyakoki. Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Nijeriya...

Mafi Shahara