DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar APC ta kalubalanci Gwamnan Filato Mutfwang da ya bayyana masu matsa masa lamba ya bar PDP

-

Jam’iyyar APC ta jihar Filato ta kalubalanci Gwamna Caleb Mutfwang da ya fito fili ya bayyana sunayen mutanen da ke matsa masa lamba ya bar jam’iyyar PDP ya koma APC.

Gwamnan ya bayyana a wani taro a fadar gwamnati da ke Jos cewa wasu jiga-jigan APC sun roƙe shi da ya shiga jam’iyyarsu, amma ya ce sai idan Allah da kuma jama’ar jihar sun yarda zai iya yanke wannan shawarar.

Google search engine

Sai dai mai magana da yawun jam’iyyar APC na riko a jihar, Shittu Bamaiyi, ya musanta ikirarin gwamnan, yana mai cewa wannan magana tana nuni ne da yadda gwamnatin Mutfwang ta gaza cika alkawuran da ta dauka ga al’umma,inda ya ce idan gaskiyane ya fito ya faɗi sunayen waɗanda ke matsa masa lamba, ya kuma bayyana su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaban Amurka Donald Trumph ya haramtawa Farfesa Wole Soyinka zuwa kasar

Gwamnatin Amurka karkashin jagorancin shugaba Donald Trump ta soke takardar izinin shiga ƙasar ga Farfesa Wole Soyinka, sanannen marubuci a duniya. Farfesa Soyinka ya bayyana hakan...

Hukumar agajin gaggawa NEMA ta karɓi ƴan Nijeriya 153 da suka makale a Chadi

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA, ta bayyana cewa ta karɓi ’yan Nijeriya 153 da suka dawo daga ƙasar Chadi, ƙarƙashin shirin Ƙungiyar...

Mafi Shahara