Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiHukumar zabe za ta hada kai da majalisar wakilan Nijeriya domin gudanar...

Hukumar zabe za ta hada kai da majalisar wakilan Nijeriya domin gudanar da sahihin zabe

Shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya bayyana aniyarsa ta yin aiki tare da Majalisar Dokoki domin tabbatar da gudanar da sahihin zabe, adalci da gaskiya a Nijeriya.

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwa da hukumar INEC ta fitar a ranar Litinin, inda Amupitan ya bayyana cewa hukumar INEC za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yan majalisa wajen sake duba dokar zabe domin tabbatar da cewa sabbin gyare-gyare za su ɗauki darussa daga zabubbukan da aka yi a baya, tare da ƙara gina amincewar al’ummar Nijeriya ga hukumar zabe.

Ya ce manufar wannan gyara ita ce rage yawan ƙorafe-ƙorafen zabe ta hanyar tabbatar da gaskiya da adalci a kowane mataki na zabe ga kowane bangare.

Ya kara da cewa, doka ce ginshiƙin tabbatar da dimokuraɗiyya, don haka dole ne ayi abinda zai hana rikice-rikicen sakamakon zabe.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata