DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kama matar da ta sace kanta don ta karbi kudin fansa daga mijinta a Nijeriya

-

Rundunar ‘yan sandan jihar Edo ta kama wata mata mai suna Chioma Success mai shekaru 27 bisa zargin shirya garkuwa da kanta don karɓar kudin fansa daga mijinta.

Mai magana da yawun rundunar, ASP Eno Ikoedem, ta ce mijin Chioma, Paul Adaniken, ya kai rahoto cewa matarsa da ɗansa sun ɓace, inda daga baya aka kira shi da wata lamba da ba a sani ba ana neman fansar Naira miliyan bitar.

Google search engine

Bincike ya gano cewa ɗan’uwan matar, Osita Godfrey, da wani abokinsu Martins Chidozie, sun taimaka wajen shirya satar. Daga baya Chioma ta amsa cewa ita ce ta tsara komai don ta karɓi kuɗi daga mijinta.

‘Yan sanda sun ce an kwato kudin fansar kuma an mika lamarin ga sashen binciken manyan laifuka na jihar don ci-gaba da bincike da gurfanarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar. Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara