DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

-

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar.

Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya ta damu da yadda Amurka ta yi hanzarin fitar da wannan matsayi bisa bayanan da ba su da tushe. Ya ce matsalolin tsaro a Nijeriya sun shafi Musulmai da Kiristoci baki ɗaya, ba wai rikicin addini ba ne.

Google search engine

DCL Hausa ta ruwaito cewa Ministan ya jaddada cewa rikicin manoma da makiyaya a Plateau da Benue ya samo asali daga tsoffin matsaloli da canjin yanayi da fari suka haifar da ƙara taɓarɓarewar. Ya ƙara da cewa gwamnati tana ƙarfafa haɗin kai da ƙasashen duniya, ciki har da Amurka, don kawo ƙarshen ta’addanci a yankin Sahel da Nijeriya baki ɗaya.

A cewarsa, hadin gwiwar da ke tsakanin Nijeriya da Amurka ya haifar da samun jiragen Super Tucano da ake amfani da su a yaƙin ta’addanci, tare da shirin karɓar sabbin jiragen yaƙi na AH-1Z Viper domin ƙarfafa rundunar sojojin sama.

Hakazalika, ya ce gwamnatin Tinubu tana bin duk hanyoyin diflomasiyya da siyasa don gyara kuskuren fahimtar da gwamnatin Amurka ta yi, tare da tabbatar da cewa ’yancin addini da rayuwar kowane ɗan ƙasa za su kasance a ƙarƙashin kariya da doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara