DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar sojin saman Nijeriya ta yi alkawarin kare rayukan farar hula lokacin gudanar da ayyuka

-

Babban hafsan sojin saman Nijeriya, Air Marshal Sunday Aneke, ya ce rundunar sojin sama za ta mayar da hankali kan kare rayukan fararen hula da gujewa mummunan hari kan farar hula yayin ayyukanta.

Aneke ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis, yayin ganawarsa ta farko da manyan hafsoshin rundunar a hedikwatar rundunar da ke Abuja, inda ya ce wannan mataki na cikin abin da shugaban Bola Tinubu ke bukata daga dakarun kasa.

Google search engine

Aneke ya ce rundunar za ta karfafa hulɗa da al’umma da kuma hadin kai da sauran hukumomin tsaro domin murkushe ta’addanci da hana maƙiya samun mafaka, sannan kuma kare rayukan fararen hula da gujewa mummunan hari shi ne ginshikin kwarewar aikin.

Hakazalika, ya kuma tabbatar wa hafsoshin cewa dukkan matakan rundunar za su bi umarnin shugaban kasa kai tsaye, tare da mayar da hankali kan inganci, tsaro da kare martabar sojin sama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara