DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya yi alwashin murkushe ta’addanci tare da karfafa dangantaka da kasashen waje

-

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya jaddada kudirin gwamnatinsa na kawar da ta’addanci da kuma karfafa dangantaka tsakanin Nijeriya da abokan hulɗarta na duniya.

Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Alhamis kafin zaman majalisar zartarwa na kasa da aka gudanar a fadar shugaban kasa, Abuja, zama na farko tun watan Yuli.

Google search engine

A cewarsa, ana tattaunawa da kasashen duniya ta hanyar diflomasiyya, kuma ya tabbatar da cewa za a murkushe ta’addanci.

Jawabin Tinubu ya zo ne kwanaki bayan shugaban Amurka Donald Trump ya sanya Nijeriya cikin jerin “Kasashen da ke da damuwa ta musamman,” abin da gwamnatin Nijeriya ta ce ba daidai ba ne wajen bayyana hakikanin matsalar tsaro.

Hakazalika Tinubu ya ce gwamnatinsa na ci-gaba da tattaunawa da kasashen duniya domin tabbatar da tsaro, zaman lafiya, da bunƙasar tattalin arzikin ƙasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Akwai yiwuwar madugun adawar Kamaru Isa Tchiroma yana Nijeriya ya boye – Rahotanni

Madugun adawar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, wanda ya kalubalanci nasarar Paul Biya, yana iya kasancewa yana a Nijeriya kamar yadda Africa Intelligence ta ce, amma...

Fusatattun matasa sun hallaka limamin masallaci a jihar Kwara bisa zargin maita

Wasu fusatattun matasa a garin Sokupkpan da ke ƙaramar hukumar Edu a jihar Kwara sun hallaka limamin masallacin yankin, Malam Abdullahi Audu, bisa zargin cewa...

Mafi Shahara