DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya yi alwashin murkushe ta’addanci tare da karfafa dangantaka da kasashen waje

-

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya jaddada kudirin gwamnatinsa na kawar da ta’addanci da kuma karfafa dangantaka tsakanin Nijeriya da abokan hulɗarta na duniya.

Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Alhamis kafin zaman majalisar zartarwa na kasa da aka gudanar a fadar shugaban kasa, Abuja, zama na farko tun watan Yuli.

Google search engine

A cewarsa, ana tattaunawa da kasashen duniya ta hanyar diflomasiyya, kuma ya tabbatar da cewa za a murkushe ta’addanci.

Jawabin Tinubu ya zo ne kwanaki bayan shugaban Amurka Donald Trump ya sanya Nijeriya cikin jerin “Kasashen da ke da damuwa ta musamman,” abin da gwamnatin Nijeriya ta ce ba daidai ba ne wajen bayyana hakikanin matsalar tsaro.

Hakazalika Tinubu ya ce gwamnatinsa na ci-gaba da tattaunawa da kasashen duniya domin tabbatar da tsaro, zaman lafiya, da bunƙasar tattalin arzikin ƙasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara