DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ka nemi yafiya bayan janye kalamanka na barazana ga Nijeriya – Barau Jibrin

-

Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Barau Jibrin, ya caccaki Shugaban Amurka, Donald Trump, bisa barazanar kai wa Nijeriya hari da ya yi,saboda zargin ana yi wa Kiristocin kasar kisan kiyashi.

Jaridar Punch ta rawaito cewa a cikin wani faifan bidiyo an gano Sanata Barau Jibrin na cewa furucin Trump ya saba wa dokar ƙasa da ƙasa bisa wannan kuduri da ya dauka.

Google search engine

Ya kuma bukaci shugaban Amurkan da ya janye kalamansa tare da bai wa Nijeriya hakuri, yana mai cewa, bai dace shugaban Amurka ya ce zai kai wa wata ƙasa hari saboda ra’ayi ba, idan akwai matsala kamata ya yi a bi ta hanyar diflomasiyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ya kamata Nijeriya ta farka daga barcin da take yi saboda barazanar da Trump ya yi mata – Bishop Kukah

Shugaban Cocin Katolika a Sokoto Archbishop Matthew Kukah ya bayyana cewa barazanar Shugaban Amurka Donald Trump kan yiwuwar kai harin ga Nijeriya a matsayin nuni...

Wata dattijuwa ta barke da kuka bayan an hanata kada kuri’a

Wata datijuwa mai shekaru 96 a duniya, Mrs. Elizabeth Onike, ta barke da kuka a rumfar zaɓe saboda an hana ta kada kuri'a a Anambara Dattijuwar...

Mafi Shahara