DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Masu sana’ar ‘DJ’ sun yi zanga-zanga ga hukumar Hisbah a Katsina

-

Masu sana’ar DJ da ke nishadantar da taron mutane a lokuttan bukukuwa sun cika makil a filin taro na Kangiwa Square a jihar Katsina, inda suka yi zanga-zanga ga hukumar Hisbah ta jihar bisa dakatar da sana’ar su da ta yi na tsawon watanni 8.
Masu sana’ar sun ma roki gwamnatin jihar Katsina da ta sa baki a bar su, su ci gaba da gudanar da sana’ar su da suka ce ba su takura wa kowa kuma ba su shiga hakkin kowa. Sun kuma koka kan cewa hukumar Hisbah din ta kwace musu kayan aiki na milyoyin Nairori.
Zanga-zangar ta su, ta yi daidai da lokacin da Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ke bude aikin fadada titin Kofar Soro zuwa Kofar Guga cikin kwaryar birnin Katsina da aka kammala kamar yadda gidan talabijin na Channels ya rawaito.
An dai ga matasan dauke kwalaye masu rubutun da ke nuna irin halin da suka ce suna ciki tun bayan dakatar musu da sana’ar da hukumar ta Hisbah ta yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara