DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dattawa ta bukaci a dauki matasa aikin tsaro domin magance matsalar tsaro

-

Majalisar dattawan Nijeriya, ta nuna damuwa kan tabarbarewar tsaro a ƙasar, tana kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya amince da daukar matasa akalla 100,000 cikin rundunonin tsaro domin ƙarfafa tsaron ƙasar da ya yi rauni.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, wannan matakin ya biyo bayan kudirin da Sanata Abdullahi Yahaya na Kebbi ta Arewa ya gabatar, inda ya ce matsalar tsaro ta kai wani yanayi mai tayar da hankali da ke bukatar gaggawar daukar matakin kasa.

Google search engine

Sanatoci irin su Abdul Ningi da Aminu Tambuwal sun ce lamarin barazana ce ga makomar kasa, suna kira ga ‘yan majalisa su guji siyasantar da batun, yayin da tsohon shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan ya nuna takaicinsa cewa duk da kudaden tsaro masu yawa, hare-hare da sace-sace na ci-gaba.

Majalisar ta kuma kafa kwamiti na wucin-gadi domin binciken yadda aka yi amfani da kudaden shirin “Safe School” duk da cewa makarantun ƙasar na kara zama cikin hadari, musamman bayan sace dalibai a Kebbi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Matukar dimokradiyya ta gaza a Nijeriya sai ya shafi fadin Yammacin Afrika – ECOWAS

Kungiyar tattalin arzikin kasashen Yammacin Afrika, ECOWAS, ta gargadi cewa duk wani rauni da dimokuradiyya ta samu a Nijeriya zai yi sanadin rushewar tsarin a...

PDP tsagin Wike ta kori Bala Muhd da Dauda Lawan, gwamnonin Bauchi da Zamfara

Jam’iyyar PDP ta kara shiga wani sabon rikici a ranar Talata bayan bangaren kwamitin zartaswa da ke goyon bayan ministan Abuja, Nyesom Wike, ya tabbatar...

Mafi Shahara