DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya tura Minista Badaru zuwa Neja don ganin an ceto daliban da aka sace

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya umurci  Ministan Tsaron kasar, Badaru Abubakar, da ya tashi kai tsaye zuwa jihar Neja domin jagorantar aikin ceto daliban makarantar St. Mary’s Catholic School da ‘yan bindiga suka sace a yankin Papiri, ƙaramar hukumar Agwara.

Umarnin na zuwa ne sa’o’i bayan da kungiyar kiristoci ta Njeriya CAN reshen jihar Neja ta tabbatar da sace ɗalibai 303 da malamai 12 a makarantar, lamarin da ya kara tayar da hankalin al’umma a fadin ƙasar saboda ƙara yawan hare-haren da ake kaiwa makarantun Arewa.

Yawan hare-hare kan makarantun ya sa gwamnatin tarayyar kasar ta umurci da a rufe makarantun sakandare mallakinta sama da 40 a fadin kasar. Yayin da gwamnatocin jihohin Katsina da Plateau suka sanar da rufe nasu makarantun firamare da sakandare.

A baya-bayan nan, Shugaba Tinubu ya tura Ministan Ƙasa a ma’aikatar tsaro, Bello Matawalle, zuwa jihar Kebbi domin ganin an ceto dalibai 24 mata na Government Girls’ Comprehensive Secondary School, Maga, da aka yi garkuwa da su a ƙaramar hukumar Danko Wasagu.

Masu sharhi na ganin cewa tura ministoci biyu manya zuwa yankuna biyu daban-daban a lokaci guda na nuna yadda matsalar tsaro ta kara kamari, tare da bukatar sabbin dabaru da matakan gaggawa. Yanzu idanun jama’a na kan yadda gwamnati za ta gudanar da aikin ceto da tabbatar da tsaro a makarantun Arewa maso yamma da tsakiya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara