DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sace dalibai na barazana ga makomarsu a Arewacin Nijeriya – Amnesty International

-

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International a Nigeria ta yi gargadin cewa yawaitar sace dalibai a makarantun arewa na iya karya ilimi, tare da jefa rayuwar yara cikin mummunar makoma.

A wata hirar da ya yi a gidan talabijin na Channels a ranar Litinin, daraktan Amnesty a Nijeriya Isa Sanusi ya ce tsananin tsoro da fargabar sace dalibai na hana su zuwa makaranta, lamarin da ke kara dagula fannin ilimi a yankin.

Google search engine

Sanusi ya bayyana cewa iyayen da ke fama da talauci musamman a karkara na fama wajen tura yaransu makaranta, a yayin da rashin tsaro da sace-sacen yara zai kara hana su yarda da aika ’ya’yansu makaranta.

Ya ce tsoron sace wa kaÉ—ai zai hana dubban yara samun ilimi a arewacin Nijeriya wanda a yanzu yaran da ba sa zuwa makaranta sun haura miliyan 12.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Kebbi ya soki rundunar sojin Nijeriya kan yadda take yakar rashin tsaro

Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris ya nuna rashin gamsuwa da tsarin da rundunar soji ke amfani da shi wajen yakar rashin tsaro yana mai kira...

Makarantun Sakandire na je-ka-ka dawo za su ci gaba da karatu – Gwamnatin Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta bai wa makarantun firamare da sakandare na je-ka-ka-dawo damar ci gaba da karatu A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta jihar ta...

Mafi Shahara