DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ina fatan shugaba Tinubu ba zai sake tsayawa takara a 2027 ba – Hakeem Baba Ahmad

-

Tsohon mai bai wa shugaba Tinubu shawara kan harkokin siyasa Dr. Hakeem Baba-Ahmed ya ce yana fatan shugaban Nijeriya ba zai sake neman kujerar shugabancin ƙasa a 2027 ba.

Ya bayyana hakane a gidan talabijin na Channels, inda ya ce Shugaba Tinubu bai nuna ƙwazo yadda ake buƙata ba wajen gyara kasar, duk da cika burinsa na zama shugaban Nijeriya.

Google search engine

A yayin tattaunawar Dr. Baba-Ahmed ya jaddada cewa tun bayan barinsa gwamnatin Tinubu, ya kan faɗi cewa shugaban ƙasar bai kamata ya sake tsayawa takara ba domin yanzu ya cimma burinsa ba tare da gudanar da mulki yadda ake tsammani ba.

Baba-Ahmed ya ce abin da aka san Tinubu da shi a baya na basira da himma babu alamun irin wannan jajircewar wajen gyaran ƙasa a halin yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara