DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An garzaya da kocin Man City Guardiola Asibiti

-

Mai horar da ‘yan wasan kungiyar Manchester City Pep Guardiola ba zai samu jagorancin kungiyar ba har na wasanni biyu da za ta buga nan gaba sakamakon wata tiyatar gaggawa da za a yi masa a gadon bayansa.
Guardiola wanda yanzu haka yana Barcelona inda aka yi masa tiyata yana kuma murmurewa ana sa ran ba zai jagoranci City ba a wasannin da za ta yi da Sheffield United a wannan Lahadi da Fulham a ranar 2 ga Satumba ba, inda mataimakinsa Juanma Lillo zai maye gurbinsa na wucin gadi.
City ta ce kocinta wanda ya jagoranci yan wasanta suka lashe kofina uku rigis a kakar da ta gabata na fama da “matsanancin ciwon baya na ” kuma tuni aka fita da shi zuwa birnin Barcelona don domin yi masa tiyata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kada mahajjaci ya rike kudin da suka wuce Riyal 60,000 a kasar Saudiyya – Jan hankalin NAHCON ga Alhazan Nijeriya

Hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON ta shawarci mahajjatan kasar da su guji daukar kudi sama da Riyal 60,000 na Saudiyya domin...

Mun yi kuskure a sakamakon da muka fitar na dalibai – Hukumar JAMB

Cikin alhini da nadamar abin da ya faru, hukumar JAMB da ke shirya jarabawar neman shiga makarantun gaba da sakandare a Nijeriya ta karbi duk...

Mafi Shahara