DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An zakuda shugabancin kamfanin mai na NNPC

-

Bayanan da ke fitowa daga kamfanin kula da man fetur na kasa NNPC na cewa an yi wa mafiyawan manyan daraktocin kamfanin ritaya daga aiki, duk da sauran watanni kusan 15 da suke da shi kafin wa’adin ritayarsu ya cika.
Wannan matakin kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, na zuwa ne kwanaki kadan bayan da kamfanin ya sanar da sallamar manyan mataimakan shugaban kamfanin su uku.
Daga cikin wadanda aka sallama, akwai Abdulkabir Ahmad da ke kula da bangaren iskar gas da Adokiye Tombomieye da ke kula da sashen albarkatun fetur.
A cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar da sanyin safiyar Talata, ya ce an dauki wannan matakin ne domin kara inganta aikinsa yadda zai zo daidai da zamani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara