DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An zakuda shugabancin kamfanin mai na NNPC

-

Bayanan da ke fitowa daga kamfanin kula da man fetur na kasa NNPC na cewa an yi wa mafiyawan manyan daraktocin kamfanin ritaya daga aiki, duk da sauran watanni kusan 15 da suke da shi kafin wa’adin ritayarsu ya cika.
Wannan matakin kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, na zuwa ne kwanaki kadan bayan da kamfanin ya sanar da sallamar manyan mataimakan shugaban kamfanin su uku.
Daga cikin wadanda aka sallama, akwai Abdulkabir Ahmad da ke kula da bangaren iskar gas da Adokiye Tombomieye da ke kula da sashen albarkatun fetur.
A cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar da sanyin safiyar Talata, ya ce an dauki wannan matakin ne domin kara inganta aikinsa yadda zai zo daidai da zamani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kada guiwarku ta yi sanyi, akwai haske a gaba – Sakon barka da sallah na Shugaba Tinubu ga ‘yan Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da cewa kasar ba ta kai inda take mafarkin kaiwa ba tukuna, amma ya roki ’yan kasa da kada...

Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya yaba wa ‘yan sandan jihar bisa dakatar da Hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yi maraba da dokar hana duk bukukuwan Sallah a jihar yayin gudanar da bukukuwan...

Mafi Shahara