DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a kashe Naira milyan 173 don samar da lantarki ta hasken rana a asibitin Dutse, jihar Jigawa

-

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da a fitar da kudi Naira milyan 173 don aikin samar da lantarki ta hasken rana a babban asibitin da ke Dutse, babban birnin jihar.
Kwamishinan yada labaran jihar Sagir Musa ya sanar da hakan ga manema labarai, inda ya ce majalisar zartarwar jihar ce ta amince da hakan bayan taron da ta gudanar a ranar Alhamis.
Kwamishinan ya ce wannan matakin ya biyo bayan kudirin Gwamnan jihar Umaru Namadi na kyautata babban asibitin jihar don samar da kiwon lafiya mai inganci ga al’ummar jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa...

Mafi Shahara