DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Katsina da Yobe ne jihohin da ba su iya rayuwa idan babu kudin FAAC na FG – Rahoto

-

Rahoton shekara-shekara na karfin hanyoyin samar da kudaden shiga na jihohi a Nijeriya ya nuna cewa akwai jihohin da idan babu daunin gwamnatin tarayya, ba za su iya tsayawa da kafafunsu ba.
Jihohin kamar yadda rahoton ya ce su ne Katsina, Kebbi, Bayelsa, Akwa Ibom, Taraba da Yobe.
Rahoton da aka fitar a ranar Litinin, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, ya nuna cewa jihohin 6 sun gaza samar da kaso 10% na kudaden shiga daga cikin gida IGR a shekarar 2022.
Kudaden shigar jihohi 36 na Nijeriya a shekarar 2022 sun kai Naira Tiriliyan 1.8, inda suka zarta na shekarar 2021 da aka samu Naira Tiriliyan 1.7.
Jihar Lagos dau ce kan gaba wajen tattara kudaden shiga a cikin gida da Naira bilyan 651 sai jihar Ogun ta biyu sai jihar Rivers ta uku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar. Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara