DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta haramta wa minista a gwamnatin Buhari rike duk wani mukamin gwamnati

-

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta dakatar da tsohuwar ministar harkokin mata a gwamnatin Buhari, Ms Pauline Tallen da karbar duk wani mukamin da ya danganci gwamnati.
A cikin hukuncin da ta yanke a ranar Litinin, kotun ta nuna rashin jin dadinta kan kalaman Pauline Tallen bayan da aka yanke hukuncin da ya danganci jihar Adamawa a shekarar bara.
A baran dai ne kotun ta yanke hukuncin cewa Aisha Binani ta APC ba ta cancanci tsayawa takarar Gwamna ba.
Daga cikin kalaman Pauline Tallen a wancan lokacin, ta ce wannan hukuncin kotu ya yi kama da hukuncin kama-karya.
Shugaban kungiyar lauyoyi ta kasa Yakubu MaiKyau a lokacin ya nemi Pauline Tallen da ta nemi afuwar ta kuma janye kalamanta, idan ba haka ba, zai maka ta kotu, amma ta kiya, dalilin da ya sa hakan ya kai su kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara