DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta haramta wa minista a gwamnatin Buhari rike duk wani mukamin gwamnati

-

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta dakatar da tsohuwar ministar harkokin mata a gwamnatin Buhari, Ms Pauline Tallen da karbar duk wani mukamin da ya danganci gwamnati.
A cikin hukuncin da ta yanke a ranar Litinin, kotun ta nuna rashin jin dadinta kan kalaman Pauline Tallen bayan da aka yanke hukuncin da ya danganci jihar Adamawa a shekarar bara.
A baran dai ne kotun ta yanke hukuncin cewa Aisha Binani ta APC ba ta cancanci tsayawa takarar Gwamna ba.
Daga cikin kalaman Pauline Tallen a wancan lokacin, ta ce wannan hukuncin kotu ya yi kama da hukuncin kama-karya.
Shugaban kungiyar lauyoyi ta kasa Yakubu MaiKyau a lokacin ya nemi Pauline Tallen da ta nemi afuwar ta kuma janye kalamanta, idan ba haka ba, zai maka ta kotu, amma ta kiya, dalilin da ya sa hakan ya kai su kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar. Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara