DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba Faransa ce ke ingiza ECOWAS daukar matakai kan Nijar ba – Ministan Tinubu

-

Ministan harkokin kasashen waje na Nijeriya Amb Yusuf Tuggar ya sanar cewa babu kanshin gaskiya a zargin da wasu ke yi cewa kasar Faransa ce ke ingiza kungiyar ECOWAS ta dauki matakan kakaba takunkumai ga kasar Nijar tun bayan juyin mulkin soji.
Kungiyar ECOWAS sai ta sanya wasu takunkumai ga kasar Nijar tun bayan da sojoji suka hambarar da gwamnatin farar hula ta Bazoum Mohammed a farko-farkon wannan shekara.
Daga cikin takunkuman akwai na rufe kan iyakar Nijeriya da Nijar da yanke wutar lantarki da katse huldar jakadanci da sauransu.
Ministan ya yi wannan furucin ne a wata zantawa da gidan talabijin na Trust Tv.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara