DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ran majalisar dinkin duniya ya baci kan kisan mutane 190 a Plateau

-

Majalisar Dinkin Duniya ta nuna bacin ran ta game da harin da wasu ‘yan ta’adda suka kai a kauyukan jihar Filato a karshen shekarar nan. 
Shugaban kula da hakkin bil adama a majalisar Dinkin Duniya Volker Turk, ya sanar da haka ne a wani jawabi da ya fitar a yammacin ranar Alhamis.
Mista Volker Turk ya nuna akwai matukar bukatar ayi gaggawar kawo karshen wannan kashe-kashen.
A cewarsa “Ina mai matukar damuwa da jeringiyar hare-haren ‘yan bindiga a kauyuka da-dama da ke jihar Filato.” 
“Ina kira ga hukumomin Najeriya su binciki wannan lamari da wuri kuma da kyau, bisa doron dokokin kare hakkin Bil Adama, kuma ayi adalci wajen hukunta wadanda aka samu da laifi a kotu.”
 “Dole a gaggauta kawo karshen wannan zalunci da yake yawon aukuwa. Sannan gwamnati ta dauki matakan kwarai wajen shawo kan asalin matsalolin tare da tabbatar da rikicin ba zai sake faruwa ba.” In ji Mista Turk. 
A halin yanzu, MDD ta bukaci gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta hana sake faruwar irin wannan ta’adi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara