DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wani fasinja ya gartsawa ma’aikaciyar Jirgi cizo.

-

 Fasinja ya gartsa wa ma’aikaciyar jirgin sama cizo

Google search engine

Wani jirgin sama a kasar  Japan da ke kan hanyarsa ta  zuwa Amurka ya koma birnin Tokyo bayan da wani fasinja da ya bugu da giya ya ciji wata mata ma’aikaciyar jirgin da hakan ya tilasta wa matukin jirgin saukar gaggawa.

An ruwaito cewa mutumin mai shekaru 55 da ake kyautata zaton Ba’amurke ne, ya ciji matar a  hannunta, inda har ya ji mata  rauni, kamar yadda mai magana da yawun kamfanin All Nippon Airways ya shaida wa kamfanin dillacin labarai na AFP.

Lamarin da ya sa matukan jirgin da fasinjoji 159 suka  zuwa filin jirgin Haneda, inda aka mika mutumin ga ‘yan sanda. 

Kafar yada labarai ta kasar Japan TBS ta ruwaito fasinjan yana fadawa masu binciken cewa “bai san ya aikata laifin ba”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa...

Mafi Shahara