DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu na rokon Super Eagles da su doke Kamaru a gasar AFCON.

-

 Tinubu na rokon Super Eagles da su doke Kamaru a gasar AFCON

Google search engine

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya roki ‘yan wasan Super Eagles da su yi duk mai yiwuwa don ganin sun samu nasara a yayin da Najeriya zasu fafata da babbar abokiyar hamayyarta, Kamaru a gobe, domin buga wasan dab da na kusa da na karshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake yi a Cote d’Ivoire. .

An isar da sakon shugaban kasar ga tawagar ta hannun ministan raya wasanni, Sanata John Owan Enoh, inda ya bukaci Super Eagles da su jajirce wajen tunkarar abokan karawarsu a wasan zagaye na 16 mai mahimmanci na gobe asabar.

Kamar yadda wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimakiya ta musamman ga sanata Enoh, Diana-Mary Tiku Nsan, ta bayyana cewa ‘yan Super Eagles sun sanar da cewa shugaban kasar na bin kungiyar ne domin yayi duk abinda ya dace a kansu, don haka dole ne su rubanya kokarinsu domin ‘yan Nijeriya da suke gida su samu Farin ciki da wannan wasa .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara