DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Talakawa sun fasa rumbun adana kayan abinci na gwamnatin jihar Kebbi da shagunan ‘yan kasuwa, sun kwasa

-

Wasu mazauna jihar Kebbi sun kai hari a rumbun adana kayan abinci na gwamnatin jihar da ke Bayan Kara cikin kwaryar Birnin Kebbi, inda suka kwashi kayan abinci.

Lamarin kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, ya faru ne a daren Asabar.
Maharan da suka yi kukan-kura suka afka a rumbun, sun kuma fasa wasu shagunan ‘yan kasuwa, suka saci kayan abinci can ma.
Kazalika, sun kuma tare wata tirela makare da kayan abinci da aka ba gwamnatin jihar Kebbi ta kayan abinci, nan ma suka wawashi hatsi.
Da ya ke ganawa da manema labarai, Muhammad Gwadangwaji, wanda shi ne shugaban ‘yan kasuwar na Bayan Kara Birnin Kebbi, ya ce matasan sun kuma banka wuta ga wasu rumbunan adana kaya ‘yan kasuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa...

Mafi Shahara