DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Karamar hukumar Danmusa na bukatar daukin gaggawa a bangaren tsaro in ji Danmusa Forum

-

Kungiyar tabbatar da shugabanci na gari ta karamar hukumar Danmusa wato (Danmusa LG Forum for Good Governnace) ta roki gwamnatin jiha da ta samar da shingen jami’an tsaro akan hanyar Yantumaki zuwa Danmusa don tababbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma. 
Shugaban kungiyar kwamarad Haruna Jafaru Danmusa ya yi wannan rokon a cikin wata sanarwa da ya fitar aka kuma raba wa manema labarai a Katsina. 
Kamar yadda ya ce hanyar Yantumaki zuwa Danmusa ta kasance cikin hatsari a halin yanzu sakamakon yawan hare-haren da ‘yan bindiga ke kai wa matafiya a hanyar wanda ke jawo rasa rayuka da kuma yin garkuwa da mutane.
Ya kara da cewa ‘yan ta’adda sun mayar da hanyar abin tsoro ga jama’ar yankin sakamakon yadda kusan duk rana ta Allah sai sun tare matafiya a hanyar.
Kwamarad Haruna jafar ya jaddada cewa kiran ya zama wajibi ta la’akari da yadda hare-haren ‘yan ta’adda ya kassara tattalin arzikin al’ummar yan’kin. 
Shugaban kungiyar ya yi amfani da damar wajen yaba ma gwamnatin jiha bisa irin kokarin da ta ke yi wajen tabbatar da kawar da matsalar tsaro a fadin jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara