DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnantin tarayya ta bayyana ranar hutu domin tunawa da Dimokuradiyya.

-

Gwamnantin tarayya ta bayyana ranar hutu domin tunawa da Dimokuradiyya.

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Laraba, 12 ga watan Yuni, 2024 a matsayin ranar hutu domin tunawa da ranar dimokradiyya ta bana.

Google search engine

Ministan harkokin cikin gida, Hon. Dr. Olubunmi Tunji-Ojo shi ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya a cikin wata sanarwa da babbar sakatariya a ma’aikatar Dr. Aishetu Gogo Ndayako ta fitar.

Ya ce, Yayin da muke bikin ranar dimokuradiyya a cikin tarihin kasarmu mai daraja, bari mu yi tunani a kan kokarin iyayenmu da suka kafa mu kuma tabbatar da cewa Nijeriya ta ci gaba da kasancewa kasa daya, amintacciyar kasa, zaman lafiya da rashin rabuwa.

Yayin da yake taya ‘yan Nijeriya murnar wannan rana, ya bukace su da su dage kan tsarin mulkin dimokradiyya.

Ministan ya bayyana cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kuduri aniyar kawo sauyi mai kyau domin farfado da tattalin arzikin kasa da inganta tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara