DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kano ya nada sabbin sarakuna 3 masu daraja ta biyu a jihar

-

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya sanar da nadin sabbin sarakuna 3 masu daraja ta biyu a jihar.
Hakan na zuwa ne bayan rattaba hannu kan sabuwar dokar da majalisar dokokin jihar ta amince da ita na kafa sabbin masarautu masu daraja ta biyu a jihar ta Kano.
A cikin wata sanarwa daga mai magana da yawun Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa, ta ce Gwamnan ya amince da nadin Alhaji Muhammd Mahraz Karaye a matsayin sabon Sarkin Karaye mai daraja ta biyu, wanda kafin nadin nasa shi ne Hakimin Rogo.
Sanarwar ta kuma ambato Alhaji Muhammd Isah Umar a matsayin sabon Sarkin Rano, wanda kafin nadin nasa shi ne Hakimin Bunkure. Da kuma Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir wanda shi ne tsohon Sarkin rusasshiyar Masarautar Gaya, da yanzu aka nada shi matsayin Sarkin Gaya mai daraja ta biyu.
Sanarwar Sanusi Bature Dawakin Tofa da DCL Hausa ta samu kwafi, ta ce nadin nasu ya fara aiki nan take.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara