DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na ba kasashen Togo da Benin wutar lantarki ta tsawon sa’o’i 24, in ji kamfanin TCN

-

Manajan Daraktan 
kamfanin rarraba wutar lantarki a Nijeriya Sule Abdul’aziz ya sanar cewa kasar na ba kasashe makwabta na Togo da Benin wutar lantarki ta sa’o’i 24 a duk rana.
Sule Abdul’aziz ya sanar da hakan a lokacin da yake jawabi a wani shirin gidan talabijin na Channels.
 Ya kara cewa Nijeriya na samar da lantarkin ga wadannan kasashe kuma suna biya yadda ya kamata. 
Sai dai ya ce ko a Nijeriya ma akwai masu samun wutar lantarki ta sa’o’i 24, musamman waɗanda ke saman tsarin Band A, suna samun ta sa’o’i 20-22, kama yadda jaridar Punch ta rawaito.
Kamfanin TCN dai ya ce an tsara ba waɗanda suke saman tsarin Band A, wutar lantarki ta sa’o’i 20-24, sai na saman Band B aka tsara ba su wutar lantarki ta sa’o’i 16-20, sai waɗanda ke saman tsarin Band C aka tsara ba su wutar lantarki ta sa’o’i 16-20 a rana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tinubu ya gargadi Alkalan Nijeriya da kada su karkata ga cin hanci ko rashin adalci

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga alkalai da sauran ma’aikatan shari’a a Najeriya da su ci gaba da zama masu gaskiya, adalci,...

PDP ta musanta zargin kirƙirar sa hannun Sakataren ta na kasa

Kwamitin zartaswa na Ƙasa na jam’iyyar PDP ya musanta zargin ƙirƙirar sa hannu da Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya yi. Mai magana da...

Mafi Shahara