DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na ba kasashen Togo da Benin wutar lantarki ta tsawon sa’o’i 24, in ji kamfanin TCN

-

Manajan Daraktan 
kamfanin rarraba wutar lantarki a Nijeriya Sule Abdul’aziz ya sanar cewa kasar na ba kasashe makwabta na Togo da Benin wutar lantarki ta sa’o’i 24 a duk rana.
Sule Abdul’aziz ya sanar da hakan a lokacin da yake jawabi a wani shirin gidan talabijin na Channels.
 Ya kara cewa Nijeriya na samar da lantarkin ga wadannan kasashe kuma suna biya yadda ya kamata. 
Sai dai ya ce ko a Nijeriya ma akwai masu samun wutar lantarki ta sa’o’i 24, musamman waɗanda ke saman tsarin Band A, suna samun ta sa’o’i 20-22, kama yadda jaridar Punch ta rawaito.
Kamfanin TCN dai ya ce an tsara ba waɗanda suke saman tsarin Band A, wutar lantarki ta sa’o’i 20-24, sai na saman Band B aka tsara ba su wutar lantarki ta sa’o’i 16-20, sai waɗanda ke saman tsarin Band C aka tsara ba su wutar lantarki ta sa’o’i 16-20 a rana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ministan yada labarai ya nesanta kansa da wani rubutu mai taken “Malagi 2027”

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a na Nijeriya, Mohammed Idris, ya nesanta kansa daga wani rubutu na siyasa mai taken “Malagi 2027”, wanda...

Wasu tsoffin ‘yan sanda sun roki Tinubu da ya sa a mayar da su aiki bayan tilasta yi musu ritaya

Wasu tsoffin jami’an rundunar ’yan sandan Nijeriya sun sake kira ga rundunar da ta bi hukuncin Kotun Kwadago ta Kasa, wadda ta bayar da umarnin...

Mafi Shahara