DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na ba kasashen Togo da Benin wutar lantarki ta tsawon sa’o’i 24, in ji kamfanin TCN

-

Manajan Daraktan 
kamfanin rarraba wutar lantarki a Nijeriya Sule Abdul’aziz ya sanar cewa kasar na ba kasashe makwabta na Togo da Benin wutar lantarki ta sa’o’i 24 a duk rana.
Sule Abdul’aziz ya sanar da hakan a lokacin da yake jawabi a wani shirin gidan talabijin na Channels.
 Ya kara cewa Nijeriya na samar da lantarkin ga wadannan kasashe kuma suna biya yadda ya kamata. 
Sai dai ya ce ko a Nijeriya ma akwai masu samun wutar lantarki ta sa’o’i 24, musamman waÉ—anda ke saman tsarin Band A, suna samun ta sa’o’i 20-22, kama yadda jaridar Punch ta rawaito.
Kamfanin TCN dai ya ce an tsara ba waÉ—anda suke saman tsarin Band A, wutar lantarki ta sa’o’i 20-24, sai na saman Band B aka tsara ba su wutar lantarki ta sa’o’i 16-20, sai waÉ—anda ke saman tsarin Band C aka tsara ba su wutar lantarki ta sa’o’i 16-20 a rana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka...

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa...

Mafi Shahara