DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An yi asarar sama da Naira biliyan 300 a yayin zanga-zangar da aka yi a watan Agusta – Kashim Shettima

-

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya ce an yi asarar sama da Naira biliyan 300 a zanga-zangar #EndBadGovernance da ta gudana a fadin kasar cikin watan Agusta.

Google search engine

Da yake jawabi a fadar shugaban kasa da ke Abuja, yayin da yake karbar yaran da aka kama yayin zanga-zangar bayan an sako su bisa umarnin shugaban kasa Bola Tinubu, Shettima ya ce an yi hasarar akasarin dukiyoyi da harkokin kasuwanci a yayin zanga-zangar.

 Ya ce duk da hujjojin da ake da su a kan yaran, shugaba Tinubu ya ba da umarnin a sake su ne saboda shi shugaba ne mai kula da bukatun al’umma.

                             

Shettima ya kuma yi kira ga gwamnoni da sauran jami’an gwamnati da su yi abinda ya kamata wajen sanya matasan masu amfani a cikin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar...

Ya kamata a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya – Femi Falana

Babban lauya kuma SAN, Femi Falana, ya bukaci a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga yara ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya, yana...

Mafi Shahara