DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An yi asarar sama da Naira biliyan 300 a yayin zanga-zangar da aka yi a watan Agusta – Kashim Shettima

-

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya ce an yi asarar sama da Naira biliyan 300 a zanga-zangar #EndBadGovernance da ta gudana a fadin kasar cikin watan Agusta.

Google search engine

Da yake jawabi a fadar shugaban kasa da ke Abuja, yayin da yake karbar yaran da aka kama yayin zanga-zangar bayan an sako su bisa umarnin shugaban kasa Bola Tinubu, Shettima ya ce an yi hasarar akasarin dukiyoyi da harkokin kasuwanci a yayin zanga-zangar.

 Ya ce duk da hujjojin da ake da su a kan yaran, shugaba Tinubu ya ba da umarnin a sake su ne saboda shi shugaba ne mai kula da bukatun al’umma.

                             

Shettima ya kuma yi kira ga gwamnoni da sauran jami’an gwamnati da su yi abinda ya kamata wajen sanya matasan masu amfani a cikin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara