DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An yi asarar sama da Naira biliyan 300 a yayin zanga-zangar da aka yi a watan Agusta – Kashim Shettima

-

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya ce an yi asarar sama da Naira biliyan 300 a zanga-zangar #EndBadGovernance da ta gudana a fadin kasar cikin watan Agusta.

Google search engine

Da yake jawabi a fadar shugaban kasa da ke Abuja, yayin da yake karbar yaran da aka kama yayin zanga-zangar bayan an sako su bisa umarnin shugaban kasa Bola Tinubu, Shettima ya ce an yi hasarar akasarin dukiyoyi da harkokin kasuwanci a yayin zanga-zangar.

 Ya ce duk da hujjojin da ake da su a kan yaran, shugaba Tinubu ya ba da umarnin a sake su ne saboda shi shugaba ne mai kula da bukatun al’umma.

                             

Shettima ya kuma yi kira ga gwamnoni da sauran jami’an gwamnati da su yi abinda ya kamata wajen sanya matasan masu amfani a cikin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai zama a San Gabriel Valley, Abiola Femi Quadri, hukuncin ɗaurin shekara 11 da wata...

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar...

Mafi Shahara