DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An bude wata makaranta da ta yi shekaru 12 a rufe a Yobe

-

 

Gwamnatin jihar Yobe ta sanar da bude makarantar sakandare ta gwamnati da ke Bara a karamar hukumar Gulani bayan shafe sama da shekaru 12 tana rufe sakamakon ayyukan ‘yan tada kayar baya.

Makarantar tare da makarantun gwamnati na Goniri da Babbangida suna aiki ne daga wani wuri na wucin gadi a Makarantar Sakandaren Gwamnati da ke Damaturu, tun 2012.

 Sabon shugaban makarantar, Mista Sulaiman Tamali, ya bayyana haka a Bara ranar Juma’a lokacin da ya ziyarci shugaban karamar hukumar Gulani, Dayyabu Njibulwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu 'yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da...

Majalisar wakilan Nijeriya ta ba gwamnonin Benue da Zamfara da shugabannin majalisunsu su wa’adin mako daya su gaggauta bayyana a gaban kwamitinta

Majalisar wakilan Nijeriya ta ba gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, da na jihar Zamfara, Dauda Lawal, tare da shugabannin majalisun dokokin jihunsu wa’adin mako guda...

Mafi Shahara