DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fada ya kaure tsakanin wasu direbobi da manajojin Dangote a Obajana

-

Wasu bayanai da DCL Hausa ta samu na cewa wani hargitsi ya kaure tsakanin wasu direbobin motocin kamfanin Dangote da ke kamfanin na Obajana a jihar Kogi da wasu manajojin kamfanin.
Majiyar DCL Hausa da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce rikicin har ya yi sanadiyyar ji wa wasu daga cikin manajojin raunuka munana.
“Da idona, na ga an karya manaja daya, amma wasu abokan aikina sun ce wadanda aka karya sun fi mutum daya”, in ji majiyar.
Wannan rikici dai na zuwa ne a daidai lokacin da direbobin motocin kamfanin na Dangote ke zargin akwai wasu daga cikin manajojin da ke yi musu kwange a wajen biyansu hakkokinsu, lamarin da ya yi sanadiyyar suka tsunduma yajin aiki na sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An mayar da ‘yan Nijeriya masu gudun hijira 26,000 gida cikin shekarar 2025 – Rahoto

Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya nuna cewa 'yan Nijeriya masu gudun hijira sama da 26,000 ne aka mayar gida daga kasashe...

An yanke wa daurarru sama da 27,000 hukunci a Nijeriya cikin shekarar 2025

Hukumar kula da gidajen ajiya da gyaran hali ta Nijeriya ta bayyana cewa akalla daurarru 27,416 ne aka yanke wa hukunci a fadin kasar cikin...

Mafi Shahara