Fada ya kaure tsakanin wasu direbobi da manajojin Dangote a Obajana

-

Wasu bayanai da DCL Hausa ta samu na cewa wani hargitsi ya kaure tsakanin wasu direbobin motocin kamfanin Dangote da ke kamfanin na Obajana a jihar Kogi da wasu manajojin kamfanin.
Majiyar DCL Hausa da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce rikicin har ya yi sanadiyyar ji wa wasu daga cikin manajojin raunuka munana.
“Da idona, na ga an karya manaja daya, amma wasu abokan aikina sun ce wadanda aka karya sun fi mutum daya”, in ji majiyar.
Wannan rikici dai na zuwa ne a daidai lokacin da direbobin motocin kamfanin na Dangote ke zargin akwai wasu daga cikin manajojin da ke yi musu kwange a wajen biyansu hakkokinsu, lamarin da ya yi sanadiyyar suka tsunduma yajin aiki na sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara