DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fada ya kaure tsakanin wasu direbobi da manajojin Dangote a Obajana

-

Wasu bayanai da DCL Hausa ta samu na cewa wani hargitsi ya kaure tsakanin wasu direbobin motocin kamfanin Dangote da ke kamfanin na Obajana a jihar Kogi da wasu manajojin kamfanin.
Majiyar DCL Hausa da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce rikicin har ya yi sanadiyyar ji wa wasu daga cikin manajojin raunuka munana.
“Da idona, na ga an karya manaja daya, amma wasu abokan aikina sun ce wadanda aka karya sun fi mutum daya”, in ji majiyar.
Wannan rikici dai na zuwa ne a daidai lokacin da direbobin motocin kamfanin na Dangote ke zargin akwai wasu daga cikin manajojin da ke yi musu kwange a wajen biyansu hakkokinsu, lamarin da ya yi sanadiyyar suka tsunduma yajin aiki na sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai zama a San Gabriel Valley, Abiola Femi Quadri, hukuncin ɗaurin shekara 11 da wata...

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar...

Mafi Shahara