DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tabbas akwai yunwa a Nijeriya amma sauki na zuwa – Shugaba Tinubu

-

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa ta mayarda hankali wajen saka jari a bangaren noma da kiwo domin magance rikicin manoma da makiyaya da kuma bunkasa tattalin arziki.
Shugaban wanda ke jawabi a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil, ya kuma jaddada cewa akwai matsalar yunwa a kasar, sai dai gwamnatin sa na kokarin ganin abubuwa sun daidaita.
Tinubu ya fadi haka ne a yayin da yake sanya hannu ga wata yarjejeniyar saka hannun jarin dala biliyan 2.5 da kamfanin JBS S.A, daya daga cikin manyan kamfunnan da ke sarrafa nama a fadin duniya.
Ya ce wannan yarjejeniya za ta magance matsalar rikici tsakanin manoma da makiyaya da ta jima tana damun al’umma a wannan nahiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata mai wakiltar Bauchi ta Arewa, Kaila Samaila, ya bar jam’iyyar PDP ya koma APC

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, Sanata Samaila ya sanar da hakan ne cikin wata wasika da ya aike wa shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio,...

Gwamnatin Tarayya ta janye darasin “mathematics” daga cikin wadanda dole dalibin Arts ya ci su a jarabawar WAEC da NECO

Ma’aikatar Ilimi ta Nijeriya ta bayyana cewa ɗaliban sakandare a fannin “Art” ba za a sake tilasta musu samun kiredit a lissafi ba a jarabawar...

Mafi Shahara