HomeUncategorizedTabbas akwai yunwa a Nijeriya amma sauki na zuwa - Shugaba Tinubu

Tabbas akwai yunwa a Nijeriya amma sauki na zuwa – Shugaba Tinubu

-

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa ta mayarda hankali wajen saka jari a bangaren noma da kiwo domin magance rikicin manoma da makiyaya da kuma bunkasa tattalin arziki.
Shugaban wanda ke jawabi a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil, ya kuma jaddada cewa akwai matsalar yunwa a kasar, sai dai gwamnatin sa na kokarin ganin abubuwa sun daidaita.
Tinubu ya fadi haka ne a yayin da yake sanya hannu ga wata yarjejeniyar saka hannun jarin dala biliyan 2.5 da kamfanin JBS S.A, daya daga cikin manyan kamfunnan da ke sarrafa nama a fadin duniya.
Ya ce wannan yarjejeniya za ta magance matsalar rikici tsakanin manoma da makiyaya da ta jima tana damun al’umma a wannan nahiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img