DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya na bin diddigin shafukan sada zumunta na ‘yan bindiga

-

Gwamnatin tarayya ta ce tana sane da yadda shafukan ‘yan ta’adda ke kara bazuwa a kafafen sada zumunta na zamani a cikin ‘yan kwanakinnan.
Wannan na zuwa ne yayin da ayyukan ‘yan bindiga ke kara karfi a shafukan sada zumunta musamman Tiktok, inda su ke nuna bindiogogi da kuma kudade zube birjik tare da yin barazanar cewa sun fi karfin gwamnati.
A wata hira da jaridar Punch, kodinetan cibiyar yaki Da ta’addanci da ke karkashin ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Maj. Gen. Adamu Laka, ya ce gwamnati na aiki tukuru domin ganin ta yaki ‘yan ta’addan ta wannan hanyar da suka É“ullo da ita.
Kodinetan ya kira ‘yan bindigar matsorata inda kalubalance su da su fito a yi gaba da gaba da jami’an tsaro ba wai labewa suna barazana ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babban layin lantarki na ‘National Grid’ ya fadi a Nijeriya

Babban layin wutar lantarki na ƙasa ya sake faɗuwa a Juma’ar nan, lamarin da ya jefa sassa da dama na Nijeriya cikin duhu. Jaridar Punch ta...

An yi ajalin magoya bayan ‘yan adawa 30, tare da kama mutum 2,000 bayan zaÉ“en Uganda – Babban hafsan sojin kasar

Babban hafsan sojin Uganda, wanda ɗan Shugaba Yoweri Museveni ne da aka sake zaɓa, ya bayyana cewa mutane 30 daga magoya bayan 'yan adawa sun...

Mafi Shahara