DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a kammala gyaran matatar man Kaduna zuwa karshen Disamba 2024

-

Manajan daraktan matatar mai ta Kaduna Dr. Mustafa Sugungun ya ce ana sa ran kammala gyaran da ake yiwa matatar Kaduna zuwa karshen shekararnan ta 2024.

Google search engine

Kamfanin mai na kasa NNPCL ne ya bayar da kwangilar gyaran wani bangare na na matatar mai ta Kaduna ga kamfanin kasar Koriya ta Kudu ‘Daewoo Engineering & Construction’ akan kuÉ—i dala miliyan 741.

Bayan kammala gyaran, matatar wadda ke aka gina domin tace ganga 110,000, za ta rika tace kashi sittin na gangar mai 66,00 a kowace rana.

A jawabinsa, babban manajan wanda ya samu wakilcin manajan sashen ayyuka na matatar Mista Emmanuel Ajiboye, a wurin kaddamar da aikin gyaran wata makaranta da kamfanin ya yi, ya ce idan aka kammala gyaran matatar za ta samar da ayyukan yi, bunĆ™asa kasuwanci da kananan sana’o’i a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed, tsohon shugaban hukumar NMMPRA Jaridar Daily Trust ta ce attajirin...

Nijeriya na bin kasashen Nijar, Togo da Benin tulin bashin kudin lantarkin da ya kai N25bn – NERC

Hukumar kula da lantarki ta Nijeriya NERC ta ce, kasar na bin kasashen Togo, Nijar da Benin bashin dala $17.8m — kimanin N25bn na lantarkin...

Mafi Shahara