DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wasu mahara sun sace mutum hudu ‘yan gida daya a jihar Kaduna

-

 

Google search engine
Al’ummar yankin Keke A dake rukunin gidajen Kaduna Millennium City sun shiga firgici, bayan sace wani yaro dan shekaru biyu tare da ‘yan uwansa mata uku da wasu ‘yan ta’adda suka yi.
An ruwaito cewa, matan wadanda aka sace ‘yan shekaru 9, da 12, da kuma 15 ne, kuma daya daga cikinsu marainiya ce. kamar yadda mahaifin yaran Yunusa Sarkin Samarin Keke ya shaidawa jaridar Dailytrust.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 9 na daren Talata, lokacin da mahaifin yaran ya tafi asibiti domin duba mahaifiyar yaran wadda ke kwance a asibiti.
Duk kokarin jin ta bakin kakakin ‘yan sandan jihar Kaduna ASP Mansur Hassan hakan ya ci tura, kuma bai mayar da sakon waya da aka tura masa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawa ta bukaci a dauki matasa aikin tsaro domin magance matsalar tsaro

Majalisar dattawan Nijeriya, ta nuna damuwa kan tabarbarewar tsaro a ƙasar, tana kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya amince da daukar matasa akalla...

Matukar dimokradiyya ta gaza a Nijeriya sai ya shafi fadin Yammacin Afrika – ECOWAS

Kungiyar tattalin arzikin kasashen Yammacin Afrika, ECOWAS, ta gargadi cewa duk wani rauni da dimokuradiyya ta samu a Nijeriya zai yi sanadin rushewar tsarin a...

Mafi Shahara