DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wasu mahara sun sace mutum hudu ‘yan gida daya a jihar Kaduna

-

 

Google search engine
Al’ummar yankin Keke A dake rukunin gidajen Kaduna Millennium City sun shiga firgici, bayan sace wani yaro dan shekaru biyu tare da ‘yan uwansa mata uku da wasu ‘yan ta’adda suka yi.
An ruwaito cewa, matan wadanda aka sace ‘yan shekaru 9, da 12, da kuma 15 ne, kuma daya daga cikinsu marainiya ce. kamar yadda mahaifin yaran Yunusa Sarkin Samarin Keke ya shaidawa jaridar Dailytrust.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 9 na daren Talata, lokacin da mahaifin yaran ya tafi asibiti domin duba mahaifiyar yaran wadda ke kwance a asibiti.
Duk kokarin jin ta bakin kakakin ‘yan sandan jihar Kaduna ASP Mansur Hassan hakan ya ci tura, kuma bai mayar da sakon waya da aka tura masa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara