DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jirgin ruwa dauke da mutane sama da 200 ya kife a jihar Neja

-

Wani mummunan hadarin jirgin ruwa da ya faru da sanyin safiyar yau Juma’a a yankin Dambo-Ebuchi na jihar Neja ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama
Wani shaidun gani da ido ya ce jirgin ya dauki mutane da suka kai 200 ciki har da mata da ‘yan kasuwa dake kan hanyar zuwa kasuwar Katcha dake ci mako-mako.
Rahotanni sun ce masu aikin ceto na ci gaba da kokarin ceto mutanen da jirgin ya kife da su, kuma zuwa yanzu an tsamo gawar mutum 8, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara